Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Yan gwaggwarmaya na zargin sojojin Siriya da kashe mutane biyar yau alhamis


Hotunan mazu zanga zanga da sojojin kasar Siriya suka harba ranar Litinin
Hotunan mazu zanga zanga da sojojin kasar Siriya suka harba ranar Litinin

Kungiyoyin kare hakkin bil adama sunce sojan kasar Sham (Syria) sun hallaka akalla mutane biyar a yau Alhamis, a daidai lokacinda tawaggar ‘yan kwamitin gani-da-ido na kasashen Larabawa suka warwatsu zuwa yankunan da gwamnati ke kokarin murkushe masu yi yi mata zanga-zangar nuna mata kyama

Kungiyoyin kare hakkin bil adama sunce sojojin kasar Sham (Syria) sun hallaka akalla mutane biyar a yau Alhamis, a daidai lokacinda tawaggar ‘yan kwamitin gani-da-ido na kasashen Larabawa suka warwatsu zuwa yankunan da gwamnati ke kokarin murkushe masu yi yi mata zanga-zangar nuna mata kyama.

Masu hakoron kare hakkokin sunce wasu daga cikin kashe-kashen gillar an yi sune a kusa da Damascus, babban birnin kasar, inda sojan suka bude wuta akan masu jayyaya da gwamnati.

Duk wannan tana faruwa ne yayinda ‘yan kwamitin gani-da-ido na kasashen Larabawan ke harramar zuwa wurare irinsu Daraa, Hama da Idlib don su gani in da gaske gwamnati take, zata daina abkawa masu yi mata zanga-zanga kuma ta saku fursunonin siyasa

Aika Sharhinka

XS
SM
MD
LG