Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Yan Kasuwa a Birtaniya Suna Gabatar Da Bukatunsu Da Suka Shafi Ficewar Tarayyar Turai


FILE - A BYD bus is displayed at a UK Trade and Investment event in London, Britain October 21, 2015. Chinese investment into low carbon London black cabs and a deal involving luxury sports carmaker Aston Martin are part of a series of business announceme

Shugabannin harkokin kasuwancin kasar Birtaniya suna kara gabatar da bukatocinsu da suka shafi ficewar kasar daga Kungiyar Tarayyar Turai-KTT, yayinda suke kokarin amfani da sakamakon zaben da aka gudanar makon da ya gabata, da ya raunana jam’iyar Conservative ta Theresa May, da ta gaza samun rinjaye kai tsaye a majalisa.

Suna kamun kafar gwamnati ta nemi dangantaka ta kut da kut da KTT fiye da yadda May tayi niyar yi da farko, wadda take kokarin ci gaba da mulki, a kalla na karamin lokaci, yayinda take fuskantar fushin jam’iyarta bisa sakamakon zaben da aka gudanar makon jiya.

Yana da wuya a iya fadin irin tasirin da rashin tabbas a harkokin siyasaryake da shi a kan shugabannin cibiyoyin kasuwanci, da kuma irin illar da zai yi ga tattalin arzikin Birtaniya idan ba a dauki matakin gaggawa ba, inji Martin, Kimanin kashi saba’in da biyu cikin dari na membobin kungiyar dake tattaunawa a madadin cibiyoyin kasuwanci, sunce ya kamata batun sake cimma wata yarjejeniyar cinikayya ta kasance abu mafi muhimmanci ga sabuwar gwamnati.

Shugabannin harkokin kasuwanci, dake daukar sakamakon zaben a matsayin tsayayya da shirin May na ficewa daga KTT, suna kira ga Firai Ministan ta tabbatar da ‘yancin zama kasar ga ‘yan kasashen turai miliyan uku da suke zaune a Birtaniya a halin yanzu, bisa hujjar cewa, suna da tasiri ga tattalin arzikin kasar.

Suna kuma so su iya harkokin kasuwanci a kasuwar daya ba tare da biyan kudin fito ba.

Facebook Forum

XS
SM
MD
LG