Shugaban yan sandan Bondo Paul Kiarie yace an harbe wasu yan zanga zangar guda uku a kauyen Siaya amma ba a kashesu ba.
An gudanar da zanga zanga a yau Juma’a a babban birnin kasar Nairobi da Mombasa da kuma Kisumu. Yan sanda sunyi amfani da hayaki mai sa hawaye a kowane birni don tarwatsa masu zanga zangar.
A jiya Alhamis ministan harkokin cikin gida Fred Matiangi ya bada umarnin hana zanga zanga a wadannan birane, inda ya fito karara yace akwai hadarin fadawa cikin rashin zaman lafiya.
Duk biranen uku, wurare ne da madugun jami’iyar adawa Raila Odinga keda rinjayi wanda ya sance kansa daga zaben zagaye na biyu da za a yi a ranar 26 ga wannan watan Oktoba, saboda hukumar zaben kasar bata canza jami’anta da yake zarginsu da shirya magudi a zaben na farko.
Facebook Forum