Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Yan Takarar Neman Shugabancin Ghana Sun Karbi Takardun Shiga Takara


Shugaban Ghana John Dramani Mahama na jami’iyar National Democratic Congress mai mulki da dan takarar babban jami’iyar adawa ta New Patriotic Party Nana Addo Dankwa Akufo-Addo da wasu yan takarar shugaban kasar sun karbi takardun shiga takara daga hukumar zaben kasar don shiga zabe ranar 7 ga watan Disamba. Masu takarar zuwa majalisa suma sun fara karbar takardunsu na shiga takara.

Masu takarar shugaban kasar zasu biya Dala Dubu 12 da dari biyar da biyar, a yayinda da ‘yan takarar majalisar zasu biya Dala Dubu 2,500 a matsayin kudin tsayawa takara, banda cika wadansu sharudda da hukumar zaben ta gindaya.
Ranakun 29 da 30 ga wannan watan Satumba hukumar zaben ta ware a hukumance da zata amshi takardun masu shiga takarar da suke sha’awar tsayawa zabe a watan Desimba inji kakakin hukumar Eric Dzakpasu.
An zargi hukumar zabe da jam’iyar NDC mai mulki da yiwa ‘yan takara zagon kasa a yunkurinsu na maida takardunsu na tsayawa takara a babban zaben da aka gudanar a shekarar Nana Konadu Agyemang Rawlings tace an gurguntar da niyarta ta wakiltar jam’iyarta ta NDP a matsayin ‘yan takarar shugaban kasa a zaben shekarar 2012.

Hawan Nasarawa, jihar Kano a Najeriya, lokacin da aka gudanar da bukukuwan Sallar Eid el Fitr
please wait

No media source currently available

0:00 0:03:44 0:00
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA
XS
SM
MD
LG