Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

‘Yan Wasan Najeriya A Wasannin Olympics A Koriya Ta Kudu Sun Burge


Ngozi Onwumere, Akuoma Omeoga da Seun Adigun.
Ngozi Onwumere, Akuoma Omeoga da Seun Adigun.

Zaratan ‘yan matan dake wakiltar Najeriya a wassanin Olympics da ake a Koriya ta Kudu na dada samun farin jini a idon duniya.

Shugaba Muhammadu Buhari na Nigeria yace ko sun sami nasara ko basu samu ba, ya shirya tsaf don karbar tawaggar ‘yanmatan nan hudu dake wakiltar Nigeria a wajen wassanin motsa jiki na Olympics wannan shekara da ake a birnin PyeongChang na Koriya ta Kudu. ‘Yan matan, wadanda suka hada da Seun Adigun, Ngozi Onwumere, Akuoma Omeoga da Simidele Adeagbo, wadanda dukkansu a Amurka aka haife su, suna kara samun kulawa ne ganin cewa, a sanadinsu, wannan ne karo na farko da Nigeria ta samu wakilci a wadanan wassanin da ake a cikin matsanancin sanyi.

Shrinmu na LABARAN WASSANI na wannan makon ya bada karin haske kan wadanan jaruman ‘yanmatan:

‘Yan Wasan na Nigeria a Wassanin Olympics a Koriya ta Kudu sun Burge - 4' 10"
please wait

No media source currently available

0:00 0:04:10 0:00

Facebook Forum

XS
SM
MD
LG