Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Yara Mata Ne Suka Kai Harin Kunar Bakin Wake Garin Maiduguri


Tashin Bom a Najeriya
Tashin Bom a Najeriya

Jami’an soja a Najeriya sunce akalla mutane 14 suka rasa rayukansu a cikin wani harin bama-bamai da wasu ‘yan kunar bakin wake suka kai a garin Maiduguri na jihar Borno dake arewa-maso-gabashin kasar.

Haka kuma jami’an sunce an raunana wasu mutane 39, kuma shedu sunce akalla biyu daga cikin maharan mata ne kuma yara Kanana ‘yan kasa da shekaru goma sha bakwai.

Wani jami’in soja, wanda yace an kai wannan farmakin ne a kusa da hanyar jiragen kasa ta Ajilari dake nan Maiduguri, ya dora laifin kai harin akan kungiyar ‘yan Boko Haram koda yake har zuwa yanzu dai ba wata kungiyar da ta fito tasa kai ta dauki alhakin ta’asar.

Hawan Nasarawa, jihar Kano a Najeriya, lokacin da aka gudanar da bukukuwan Sallar Eid el Fitr
please wait

No media source currently available

0:00 0:03:44 0:00
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA
XS
SM
MD
LG