Majalisar Dinkin Duniya ta kaddamar da wani shiri na yaki da bayanan bogi da ake yadawa a shafukan sada zumunta wadanda suka shafi annobar coronavirus.
Sakataren Majalisar Antonio Guteress ya fada a wata sanarwa da ya fitar a jiya Alhamis cewa, “babu yadda za mu nade hannayenmu muna kallo wasu suna yada karerayi tare da jefa fargaba a zukatan mutane da kuma kiyayya.
A kwanakin baya, Guterres ya nuna damuwa kan yadda matsalar nuna wariya, da kalaman batanci da kuma nuna kyama dangane da cutar coronavirus, suke yaduwa a yanar gizo.
Tun dai bayan bullar cutar COVID-19, ake ta samun yaduwar labaran da ke danganta cutar da wata makarkashiya a shafukan yanar gizo da sakonnin da ake aikawa ta hanyoyin tes na shafukan sada zumunta.
Wannan shirin da majalisar ke shirin kaddamarwa, na kokarin ya kai ga miliyoyin mutane a duk fadin duniya inda za a yada shi cikin harsuna da dama akan cutar COVID-19.
Shirin wanda aka mai taken “verified” wato abinda aka tabbatar, zai dogara ne ga dumbin bayanan da za a rika watsawa a kullum a sassan duniya, wanda zai zo a kimtse domin yadawa a shafukan sada zumunta dauke da rahotannin da Majalisar Dinkin Duniya da Hukumar lafiya ta WHO suka tabbatar da sahihancinsu.
Za ku iya son wannan ma
-
Fabrairu 18, 2021
Kungiyar Kasuwanci ta Duniya Na Bukatar Sabon Salon Gudanarwa-Dr. Ngozi
-
Fabrairu 18, 2021
Guterres Ya Yi Kiran a Samar Da Tsarin Bai Daya Na Rigakafin Coronavirus
-
Fabrairu 16, 2021
Kungiyar WTO Ta Gabatar Da Sabuwar Shugaba Ngozi Okonjo-Iweala
-
Fabrairu 16, 2021
Hukumar Lafiya Ta Duniya (WHO) Ta Aminta Da Riga Kafin AstraZeneca
Facebook Forum