An Bada umurnin Daukar Duk Wani Matakin Wanzar Da Zaman Lafiya A Najeriya

Gawarwakin mutane a zube a Maiduguri a kusa da wata tankar yakin sojoji

Shugaba Goodluck Jonathan na Najeriya ya bada umarnin daukar dukan matakan da suka kamata da zasu kaiga samar da zaman lafiya mai dorewa a jihohin Borno da Yobe da kuma Adamawa inda aka kafa dokar-ta-baci.
Shugaba Goodluck Jonathan na Najeriya ya bada umarnin daukar dukan matakan da suka kamata da zasu kaiga samar da zaman lafiya mai dorewa a jihohin Borno da Yobe da kuma Adamawa inda aka kafa dokar-ta-baci.

Shugaban Najeriyan yace duk da yake jami’an sojoji ne zasu kula da harkokin tsaro a jihohin, shugaba Jonathan yace shugabannin siyasa na jihohin zasu ci gaba da rike mukamansu.

Shugaban kasar ya kuma bada umarnin tura karin sojoji a jihar da nufin tabbatar da kiyaye doka da oda.

Your browser doesn’t support HTML5

Jawabin Shugaba Goodluck Jonathan-1:45