ZABEN2015: An Fara Musayar Kalamai a Jihar Taraba

Jihar Taraba

Yanzu haka, wata sabuwa ta kunno kai a faggen siyasar jihar Taraba, inda ake kaiwa 'yan takara hari yayin gangamin kamfe, batun da ke kara tada hankula.

Cikin wadanda suka hadu da fushin yan siyasan har da tawagar mukaddashin gwamnan jihar dana 'yan takarar PDP, da SDP.

Yanzu haka an soma musayan kalamai a tsakanin jam’iyyun siyasa, a jihar Taraba, game da harin da ake kaiwa ‘yan takarar yayin gangamin kamfe wanda a wasu lokuta kan jawon hasaran rayuka.

Duk jam’iyyun jihar na zargin juna dagane da hare-haren dake faruwa a wuraren kamfe.

Mukaddashin Gwamnan jihar Sani Danladi, daya ke jawabi kan hare-haren yace an ci masa mutunci, amma yayi hakuri, ya yafewa kowa, yace amma duk wanda yace ba zaiyi biyayya ga Gwamnati ba toh zai gamu da hukuma.

Your browser doesn’t support HTML5

An Fara Musayar Kalamai a Jihar Taraba - 3'28"