An Kubutar Da Dalibai 340 Da 'Yan Bindiga Suka Sace A Katsina

Daliban Da Aka Sace

Rahotanni daga jihar Katsina na bayyana cewa an ceto yara dalibai 'yan makarantar sakandare da aka sace a Kankara.

Labarai daga majiya mai karfi sun bayyana cewa an sami nasarar kubutar da dalibai 340 da aka sace su a makarantar sakandaren kwana da ke garin Kankara ta jihar Katsina a ranar Juma'a da ta gabata.

Rahotannin sun bayyana cewa an sami nasarar kwato wadannan daliban ne a wani yankin jihar Zamfara. Gwamnatin jihar ta Katsina ta tabbatar da cewa yanzu haka wadannan daliban suna hannun karkashin kulawar ta kuma suna cikin koshin lafiya.

Daliban Da Aka Sace

Nan ba da jimawa ba ake sa ran gwamnan jihar ta Katsina Alh. Aminu Bello Masari zai karbi wadannan daliban da kuma bayyana wa duniya halin da suke ciki.

Ga rahoton da wakilin Muryar Amurka Umar Faruk Musa ya hada muna cikin sauti.

Your browser doesn’t support HTML5

An Samu Nasarar Kubutar Da Dalibai 340 Da 'Yan Bindiga Suka Sace

Your browser doesn’t support HTML5

Daliban Sakandaren Kankara: Yadda Aka Yi Na Kubuta

Karin bayani akan: Boko Haram, sojoji, da jihar Katsina.