Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

MATSALAR TSARO: Majalisa Ta Yanke Kauna Da Hafsoshin Soja


Babban Hafsan Sojojin Najeria Janar Tukur Yusuf Burutai Ya Ziyarci Sansanonin Sojojin Najeriya.
Babban Hafsan Sojojin Najeria Janar Tukur Yusuf Burutai Ya Ziyarci Sansanonin Sojojin Najeriya.

Majalisar Dokokin Najeriya ta ce dole hafsosin tsaron kasar su sauka, saboda gazawarsu wajen samar da tsaro.

A daidai lokacin da takkadama tsakanin bangaren zartarwa da na majalisar dokokin Najeriya ke neman sauya salo, ’yan majalisar dattawa sun yanke kauna akan manyan hafsoshin tsaron kasar sakamakon abin da suka kira kasawar su wajen tsaron ‘yan kasa.

Lamarin dai ya kara kamari biyo bayan sace yara ‘yan makarantan sakandare a Kankara ta jihar Katsina da mayakan boko haram suka dauki alhaki.

Laftanal Janar Tukur Yusuf Buratai Ya ziyarci Garin Gudumbali Dake Damasak.
Laftanal Janar Tukur Yusuf Buratai Ya ziyarci Garin Gudumbali Dake Damasak.

’Yan majalisar dattawan Najeriya sun kara jadada matsayinsu na cewa wajibi ne gwamnatin tarayya ta saurari al’ummar kasar, ta bangaren sauya hafsoshin tsaron saboda kasawarsu wajen sauke nauyin da ya rataya a wuyansu na tsaron rayuka da dukiyoyi.

Sanata Kashim Shattima kuma tsohon gwamnan jihar Borno ya bayyana cewa duk da yake suna kaunar shugaban kasa Muhammadu Buhari, amma ba za su zura ido suna gani ana aikata ba daidai ba game da yadda gwamnatin tarayya ke ci gaba da rike manyan hafsoshin tsaro duk da cewa sun gaza wajen aikin su.

Shattima ya ce kamata ya yi a jarraba wasu manyan hafsoshi da za su ja ragamar tsaro kamar yadda shugabannin baya su ka yi.

yadda-daya-daga-cikin-daliban-da-aka-sace-a-katsina-ya-kubuta

ana-neman-hanyar-ceto-dalibai-ba-tare-da-amfani-da-karfin-soja-ba-masari

iyaye-sun-bayyana-fargabarsu-kan-garkuwa-da-daliban-najeriya

Takwarorin su na majalisar wakilai ma sun goyi bayan matakin ajiye aikin manyan hafsoshin tsaro, duk da yake an sami rarrabuwar kawuna tsakanin ‘yan majalisar wakilan daga jam’iyyun APC da PDP kan batun tsige shugaban kasa.

To sai dai mai magana da yawun shugaban kasa, Mallam Garba Shehu ya yi bayani a kan matakan da gwamnati ke dauka inda ya bukaci a ba gwamnati lokaci.

mutane a harabar makarantar da aka sace dalibai
mutane a harabar makarantar da aka sace dalibai

Majalisar wakilai dai ta bukaci hukumomin kasar su aiwatar da matakin gaggawa kan kare makarantu domin tsaron rayukan dalibai da malaman su daga hare-haren ‘yan ta’adda.

Saurari cikakken rahoton Halima Abdulra’uf cikin sauti

Majalisa ta yanke kauna da jami'an tsaro:3:00"
please wait

No media source currently available

0:00 0:04:22 0:00

Daliban Sakandaren Kankara: Yadda Aka Yi Na Kubuta
please wait

No media source currently available

0:00 0:03:39 0:00

Iyaye Sun Bayyana Fargabarsu Kan Garkuwa Da Daliban Najeriya
please wait

No media source currently available

0:00 0:03:00 0:00

Karin bayani akan: Boko Haram, sojoji, da jihar Katsina.

  • 16x9 Image

    Grace Alheri Abdu

    Grace Alheri Abdu  babbar Edita ce (Managing Editor) a Sashen Hausa na Muryar Amurka wadda ta shafe sama da shekaru 30 tana aikin jarida. Tana da digiri na biyu a fannin dokoki da huldar diplomasiyar kasa da kasa, da kuma digiri na biyu a fannin nazarin addinan al'adun gargadiya na kasashen Afrika.

XS
SM
MD
LG