Mahajjatan Najeriya na Shirin Komawa Gida

Mahajjatan hajjin bana sun kammala aikin wannan shekara, sun ma fara shirye-shiryen komawa gida, inda wadansu alhazan suka dukufa wajen sayen kayan tsaraba da maraba.

A wata hira da wakilin Muryar Amurka Ibrahim Abdulaziz yayi da wani mahajjati mai suna Alhaji Dan Kawu Jagada daga Jihar Adamawa, wanda ya baiyana farin cikinsa da kammala aikin hajin bana, inda ma yace “na ji farin ciki, ba ni kadai ba, duk wani mai tunin arewacin Najeriya sa yakumace duk wani mutumin Arewacin Najeriya daya je Saudiyya, ya tsaya yayi addu’a Allah Ya kare mu”.

Akwai kuma wasu rahotanni ma dake cewa wasu mahajjatan sun sami hatsari a inda wani mahajjati ya rigamu gidan gaskiya, biyo bayan kade shi da mota tayi a Minna.

Babban likitan dake kula da mahajjatan Nageriya Dr. Ibrahim Kana ya kara tabbata da afkuwar hatsarin, ya kuma ce hukumomin Saudiya sun nuna yabonsu a bana ga goyon bayan da ‘yan Nageriya suka basu a harkokin Hajji.

Your browser doesn’t support HTML5

Mahajjatan Najeriya na Shirin Komawa Gida - 3'42"