'Yan Takarar Shugaban Kasar Amurka Za Su Yi Muhawarar Karshe Kafin Zabe

'Yan Takatarar Shugaban Kasar Amurka Donald Trump da Joe Biden.

Yau alhamis za a gudanar da muhawara ta biyu kuma a karshe tsakanin 'yan takarar shugaban kasar Amurka kafin zaben shugaban kasa da za a gudanar ranar uku ga watan Muwamba.

Dan takarar shugaban kasa na jam'iyar Republican Donald Trump, da abokin karawarsa na Democrat tsohon mataimakin shugaban kasa Joe Biden, zasu fafata a wata mahawara da yammacin yau Alhamis, kwanaki 12 kafin zaben kasar a ranar uku ga watan Disamba na wani wa’adin shekaru hudu a fadar White House.

‘Yan takarar biyu da dukkanin su suka haura shekaru 70 sun yi ta yiwa juna katsalandan a mahawarar sa’o’i 90 da aka gudanar a karshen watan Satumba da kwararru a harkokin siyasar Amurka suka kwatanta da mafi muni a muhawarar da Trump yafi Biden yin katsalandan.

Muhawarar 'Yan takatar Shugaban kasar Amurka Donald Trump da Joe Biden

yan-takarar-shugaban-kasar-amurka-sun-tafka-muhawara

trump-da-biden-sun-yi-musayar-zafafan-kalamai-a-muhawararsu

zaben-amurka-na-2020-muhawarar-mataimakan-yan-takara

Amma a wannan karo, hukumar shirya mahawarar shugaban kasa zata rufe abin maganar dan takarar yayin da daya ke maganar mintu biyu na amsa tambayoyi a kan muhimman batutuwa shida da mai jagorantar mahawarar Kristen Walker ta labaran NBC zata rika gatarwa.

shirye shiryen da aka yi da kuma yadda za a gudanar da muhawarar wadda za a yi a wata jami’a a Nashville dake jihar Tannessee sun sauya a kan abin da ya faru a mahawarar farkon. An soke mahawara ta biyu da aka shirya yi a makon da ya gabata bayan da Trump ya kamu da coronavirus aka kuma kwantar dashi a asibiti kwanaki uku.