Ana fargabar cewa daliban Najeriya da dama ne ba za su sami damar rubuta jarabawar share fagen shiga jami'a ta JAMB ba a shekarar karatu ta 2021/2022, sakamakon dagewar da hukumar shirya jarabawar ta JAMB ta yi, na sanya lambar katin zama dan kasa wato NIN, a cikin sharudan yin rijistar jarabawar.