Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

A BARI YA HUCE: Labarin Addu'ar Wani Banufe Akan Bahadeje A Makka


Baba Yakubu Makeri da Grace Alheri Abdu
Baba Yakubu Makeri da Grace Alheri Abdu

Washington, D.C. - A wannan shirin za ku ji labarai biyu na wani banufe da ya je Makka yana addu'a, sai wani bahadeje ya tsaya bayansa yana cewa ka ninka min duk abin da banufen nan ke roka, sai banufe ya ce Allah ka nakasa min idona daya wato bahadeje ya makance kenan.

Sai kuma labarin wanda ya je sayen ragon layya, bayan kammala ciniki, mai sayen rago ya kirga kudi kafin ya bayar sai rago ya fizge kudin ya tattauna ya hadiye, tambaya itace, wanene ke da bashi?

Saurari cikakken shirin da Alheri Grace Abdu da Baba Makeri suka gabatar:

A BARI YA HUCE: Labarin Addu'ar Wani Banufe Akan Bahadeje A Makka
please wait

No media source currently available

0:00 0:24:41 0:00

  • 16x9 Image

    Grace Alheri Abdu

    Grace Alheri Abdu  babbar Edita ce (Managing Editor) a Sashen Hausa na Muryar Amurka wadda ta shafe sama da shekaru 30 tana aikin jarida. Tana da digiri na biyu a fannin dokoki da huldar diplomasiyar kasa da kasa, da kuma digiri na biyu a fannin nazarin addinan al'adun gargadiya na kasashen Afrika.

XS
SM
MD
LG