Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

A BARI YA HUCE: Labarin Mai Santin Rake Da Mai Santin Shinkafa, Afrilu, 10, 2021


Alheri Grace Abdu
Alheri Grace Abdu

A wannan makon bakon shirin A Bari Ya Huce, dan jarida Ado Hazzad ya bada labarai biyu na gwanayen santi.

Mutum na farko ana bude baki bara, bayan ya yi laumar shinkafa sai ya daga kai yace, "shin nawa ake saida buhun siminta a shekara ta dubu dari tara da tamanin?" sai abokan su ka ce "ko dai nawa a ke sayar da buhun shinkafa?"

Na biyu kuma yana shan rake lokacin da kotu ta soke zaben gwamnan jihar Anambra Chris Ngige sai ya ce "wai tsohon gwamnan jihar Anambran da aka tsige ina zai tafi yanzu?" sai abokan suka ce "ba sai ya tafi Makarfi ba ya yi noman rake?"

Saurari cikakken shirin:

A Bari Ya Huce: Labarin Mai Santin Rake Da Mai Santin Shinkafa 24: 00"
please wait

No media source currently available

0:00 0:24:08 0:00


  • 16x9 Image

    Grace Alheri Abdu

    Grace Alheri Abdu  babbar Edita ce (Managing Editor) a Sashen Hausa na Muryar Amurka wadda ta shafe sama da shekaru 30 tana aikin jarida. Tana da digiri na biyu a fannin dokoki da huldar diplomasiyar kasa da kasa, da kuma digiri na biyu a fannin nazarin addinan al'adun gargadiya na kasashen Afrika.

XS
SM
MD
LG