Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

A Benin An Fara Kidayar Kuri'un Zaben Jiya


Wasu masu kada kuri'a a kasar Benin
Wasu masu kada kuri'a a kasar Benin

An fara kirga kuri’u bayan kamala zabe jiya Lahadi na zaben wanda zai maye gurbin Thomas Boni Yayi, wanda ya sauka bayan kamala wa’adin mulki biyu, ya bar ‘yan takara 33 suna neman shugabancin kasar dake yammacin Afrika.

Boni Yayi ya bar ofis bayan kamala wa’adin mulkinsa biyu, tare da jadada kasancewar Benin abin koyi a fannin damokaradiya a nahiyar dake fama da fadi tashin siyasa inda shugabanni suke yiwa kundin tsarin mulkin kasashensu gyaran fuska domin su ci gaba da zama kan karagar mulki.

Ya shaidawa manema labarai lokacin da ya kada kuri’arsa cewa, yabar kadar tsitsiya madaurinki daya.
Idan babu dan takrar da ya sami rinjaye a zagayen farko, za a gudanar da zagaye na biyu cikin makonni biyu.

XS
SM
MD
LG