Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Amurka Na Fargabar Mummunan Tashin Hankali A Sashin Kan Iyakar Sassan Sudan


Wasu 'yan gudun hijirar rikicin yankin Abyei kenan.
Wasu 'yan gudun hijirar rikicin yankin Abyei kenan.

Amurka na nuna damuwarta da yadda ake ta girke askarawa a yankin Abyei na Sudan da ake takaddama a kai.

Amurka na nuna damuwarta da yadda ake ta girke askarawa a yankin Abyei na Sudan da ake takaddama a kai.

Kakakin Ma’aikatar Harkokin Wajen Amurka Mark Toner, ya fadi cewa Amurka ta yi tir da girke mayaka a bangarorin biyu. Ya ce wannan fito-na-fito ne mai hadari kuma ba abin yadda ba ne.

Kakakin yace tabarbarewar al’amura a yankin zai kawo nakasu ga yarjajjeniyar zaman lafiyar da kasar ta cimma a 2005.

A farkon wannan satin, sojoji daga bangarorin arewa da gudu sun gwabza a yankin na Abyei, wanda hakan ya yi sanadin mutuwar mutane 14. Arewaci da kudancin Sudan sun sha zargin juna da tura dinbin sojoji a yankin na Abyei.

Yankin na Abyei mai arzikin man fetur ya kasance fagen daga a yakin basasar Sudan na tsawon shekaru 21.

Kudancin Sudan ya kada kuri’ar bukatar ballewa daga arewaci da gagarimin rinjaye a kuri’ar raba gardamar da aka gudanar a watan Janairu, wadda shugabannin bangaren arewa su ka ce za su mutunta. To saidai fa har yanzu ba a tantance makomar yankin na Abyei ba.

XS
SM
MD
LG