Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Amurka Ta Karyata Batun Kwace Birnin Manbij Da Syria Tace Ta Yi


Shugaba Trump Da Sojojin Amurka

Duk da ikirarin da rundunar yankin Manbij ke yi cewa ta kwace ikon yankin, sakamon gagarumin janyewar sojojin Amurka a Syria, jami’an sojin Amurka sun ce ya zuwa yanzu babu wani abin da ya canza a wurin.

Amurka a jiya Juma’a ta yi watsi da batun soijojin Syria sun kwace ikon birnin Manbij dake arewa maso gabashin Syria, inda ake bata kashi tsakanin mayakan Kurdawa masu samun goyon bayan Amurka da sojojin Turkiya, bisa bukatar Kurdawan Syria.

A cikin wata sanarwa, ma’aikatar sojin Syria tace dakarunta sun kwace muhimman wurare kuma ta kara da tabbatarwa al’ummar yankin cewa akwai cikakken tsaro ga ‘yan Syria da ma wasu dake zaune wurin.

Sai dai rundunar hadin gwiwa a jagorancin Amurka dake yaki da kungiyar IS a wurin ta maida martani ta sakon Twitter tana fadar cewa babu alamar gaskiya a wannan maganar.

Kana rundunar hadin gwiwar ta kara da yin kira ga duk wani mahaluki da ya mutunta ‘yancin Manbij da kuma tsaron mutaneta.

Facebook Forum

An Sami Karuwar Farashin Kayayyaki A Jamhuriyar Nijar
please wait

No media source currently available

0:00 0:03:42 0:00
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA
Shiye-Shiryen Shiga Watan Azumi A Kasar Ghana
please wait

No media source currently available

0:00 0:03:56 0:00
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA
Ziyarar Sakatare Blinken A Jamhuriyar Nijar
please wait

No media source currently available

0:00 0:02:57 0:00
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA
Al'umomi Sun Koka Game Da Tashin Farashin Kayayyaki
please wait

No media source currently available

0:00 0:03:57 0:00
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA
XS
SM
MD
LG