Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Amurka Bata Yi Na'am da Ikirarin Sojin Najeriya Ba


Hoton 'yan matan Chibok d 'yan binidga suka sace.
Hoton 'yan matan Chibok d 'yan binidga suka sace.

Kakakin ma'aikatar harkokin wajen Amurka Jen Psaki, tace idan har Amurka ta san inda ake garkuwa dasu ba zata fada ba.

Ma’aikatar harkokin wajen Amurka tace bata da wata kafa mai zaman kanta da zata gaskanta ikirarin da gwamnatin Najeriya tayi cewa ta san inda ake garkuwa da ‘yan mata ‘yan makaranta da ‘yan binidga na kungiyar Boko Haram suka sace suke rike dasu.

Kakakin Maikatar harkokin wajen Amurka Jen Psaki, ta fada jiya talata cewa, ko da Amurka ta san inda suke, ba zata fito fili ta bayyana ba.

Haka kuma kamar yadda hukumomin Najeriya suka fadi, ita ma Amurkan watakil ba zata yi garajen daukan matakan kubutar da su ba saboda tsaron lafiyar ‘yan matan.

A cikin watan jiya ne kungiyar ta Boko Haram ta sace kimanin yara ‘yan makaranta su kusan dari uku a Chibok cikin jihar Borno.

Shugaban Najeriya Goodluck Jonathan ya ce gwamnatins a ba zata tattauna da ‘yan kungiyar ba, daga nan ta bukaci a sako sub a tareda wani sharadi ba.

Wani jami’I a yankin Chibok ya gayawa wani ma’aikacin VOA cewa shugaban kasa ya amince da bukatar kungiyar Boko Haram na ganin an saki ‘yan kungiyar da gwamnati take tsare dasu, su kuma su saki ‘yan matan.

Labarai masu alaka

XS
SM
MD
LG