Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

An Jefi Motar Shugaban Kungiyar Matasan Arewa


.
.

An tashi baram-baram daga wani taron da aka kira na matasa a Kaduna, bisa zargin cewa an shirya fakewa da taron ne don goyon bayan shugaba Goodluck Jonathan

Matasan da aka kira zuwa wurin wani taron da ake zaton na tattauna matsalolin matasan arewa ne a Kaduna, sun bi shugaban taron da ihu, daga bisani kuma suka kewaye motarsa da jifa a bayan da ya bayyana gare su cewa watakila makasudin wannan taro shi ne neman nunawa shugaba Goodluck Jonathan cewa yana da goyon bayan matasan.

Mutane da yawa sun mike suka fice daga wurin wannan taron, wasu kuma suka fara ihun nuna rashin yarda a bayan da shugaban Kungiyar Matasan Arewa, Jibril Lawal Tafida, ya fara tabo batun cewa su na zama tare da shugaba Jonathan kuma zai mika koke-koken matasan na arewa gare shi.

Da yawa daga cikin matasan da suka tattauna da wakilinmu sun ce ba abinda aka ce musu za a yi a wurin taron ba ke nan. Ahmed Hassan Rufa'i yace an kira su ne bisa hujjar cewa wai za a tattauna samun hadin kan matasan arewa ne, amma sai daga baya suka gane cewa wai a kan a goyi bayan shugaba Jonathan ne.

Haka kuma yace an yi a kan za a tattauna matsalolin arewa, amma kwatsam sai suka ji mai kiran taron a jawabinsa ya koma batun cewa yana tare da shugaba Jonathan kuma zai kai kukarsu gabansa.

Sai dai malam malam Jibril Tafida ya musanta cewa ya kira taron ne don neman goyon baya ma shugaba Goodluck Jonathan.

Ga cikakken rahoton da wakilinmu Lawal Isa Ikara, ya aiko mana daga Kaduna.

please wait

No media source currently available

0:00 0:03:22 0:00
Shiga Kai Tsaye
XS
SM
MD
LG