Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Malamai Kimanin 30 Aka Kashe A Jihar Borno


Shugaban kungiyar malaman firamare a Jihar Borno, Comrade Bulama Abiso, yace hare-haren 'yan bindiga sun kashe malamai kimanin 30 a fadin jihar

An kashe malaman makarantun firamare da na sakandare kimanin 30 a Jihar Borno a hare-haren da 'yan bidniga suka rika kaiwa a cikin jihar a 'yan watannin nan,

Shugaban Kungiyar Malaman Makarnatun Firamare a Jihar Borno, Comrade Bulama Abiso, shi ne ya bayyana hakan a wajen bukin ranar tunawa da malamai ta duniya da aka gudanar a garin Maiduguri.

Ya roki gwamnatin jihar Borno da hukumomin tsaro da su tabbatar da daukar karin matakan kare malamai, wadanda suke sadaukar da rayukansu domin koyar da dalibai a jihar.

haka kuma, Comrade Bulama Abiso, ya roki gwamnati da ta duba batun albashi mafi kankanci da ya kamata a rika biyan malamai, yana mai fadin cewa a hukumance, su na goyon bayan matakin tacewa da tabbatar da malaman makarantun da gwamnati take aiwatarwa.

Wakilin Sashen Hausa, Haruna Dauda Biu, ya aiko da cikakken bayanin wannan buki a bayan ya tattauna da shugaban kungiyar malaman.

please wait

No media source currently available

0:00 0:03:27 0:00
Shiga Kai Tsaye
XS
SM
MD
LG