Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

An Yankewa Wani Mutum Hukumcin Daurin Shekaru 45 Domin Satar Wayar Gwamna


'Yan Sandan Najeriya sun mamuke wani mutum
'Yan Sandan Najeriya sun mamuke wani mutum
Kotun dake zama a Osogbo jihar Osun ta yankewa wani mutum mai suna Kelvin Igbodalo hukumcin daurin shekaru 45 a gidan yari sabili da satar wayar salula ta gwamnan Rauf Aregbesola da aka kiyasta kudinta a kan Naira 50,000 a lokacin rantsar da shi.

An tuhumi Kelvin da aikata laifuka shida da suka hada da yin sojan gona, da sata, da zamba cikin aminci da kuma damfara.

Mutumin da ake tuhuma da satar wayar ya yi amfani da ita wajen damfarar Oba Gabriel
Adekunle Aromolara, Owa Obokun na Ijesha naira 500,000, yayinda ya kuma damfani wani Naira 200,000.

Wakilinmu Hassan Umaru Tambuwal ya nemi ra’ayoyin wadansu mazauna jihar Osun dangane da wannan hukumcin.

please wait

No media source currently available

0:00 0:02:33 0:00
Shiga Kai Tsaye
  • 16x9 Image

    Grace Alheri Abdu

    Grace Alheri Abdu  babbar Edita ce (Managing Editor) a Sashen Hausa na Muryar Amurka wadda ta shafe sama da shekaru 30 tana aikin jarida. Tana da digiri na biyu a fannin dokoki da huldar diplomasiyar kasa da kasa, da kuma digiri na biyu a fannin nazarin addinan al'adun gargadiya na kasashen Afrika.

XS
SM
MD
LG