Kwamitin da gwamnonin arewacin Najeriya suka kafa domin bincike masababin tashe tashen hankali da ake fuskanta a yankin ya mika rahotonsa.
Kwamitin da Jakade Zakari Ibrahim ya jagoranta ya mika rahoton ne bayan ya shafe watanni takwas yana aiki.
Daga cikin matsalolin da kwamitin ya tarar akwai, talauci, da rashin aikin yi musamman tsakanin matasa.
A cikin hirarsu da wakiliyarmu Madina Dauda shugaban kwamitin ya bayyana kwarin guiwa cewa gwamnonin zasu maida hankali wajen aiwatar da shawarwarin kwamitin, yayinda a nasu bangaren gwamnonin suka yi kira ga al’umma su bada hadin kai domin nasarar shirin.
Kwamitin da Jakade Zakari Ibrahim ya jagoranta ya mika rahoton ne bayan ya shafe watanni takwas yana aiki.
Daga cikin matsalolin da kwamitin ya tarar akwai, talauci, da rashin aikin yi musamman tsakanin matasa.
A cikin hirarsu da wakiliyarmu Madina Dauda shugaban kwamitin ya bayyana kwarin guiwa cewa gwamnonin zasu maida hankali wajen aiwatar da shawarwarin kwamitin, yayinda a nasu bangaren gwamnonin suka yi kira ga al’umma su bada hadin kai domin nasarar shirin.
-
Grace Alheri Abdu
Grace Alheri Abdu babbar Edita ce (Managing Editor) a Sashen Hausa na Muryar Amurka wadda ta shafe sama da shekaru 30 tana aikin jarida. Tana da digiri na biyu a fannin dokoki da huldar diplomasiyar kasa da kasa, da kuma digiri na biyu a fannin nazarin addinan al'adun gargadiya na kasashen Afrika.