Manyan lauyoyin jihohin karkasin jagorancin babban lauyan jihar California sun shigar da kara a ranar Litinin a wata kotun dake gundumar arewancin California.
Karar da su shigar na cewar ayyana dokar ta bacin ya sabawa dokoki da ma kundin tsarin mulkin kasar, haka kuma zai cutar da jihohi da mazauna cikin su idan aka dauki kudade daga fannonin yaki da miyagun kwayoyi da ayyukan gine-ginen sojoji da ma wasu ayyukan hukumomin tsaro, domin wannan aiki.
Kararrakin sun yi kira ga kotu ta hana gwamnatin Trump kwata-kwata a kan aniyar ta ta karkatar da kudaden asusu zuwa ginin bango da take niyar yi ko kuma a hana ta gina bangon ba tare da majalisun tgarayya sun bata kudi ba.
Facebook Forum