Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Ana Horas da ‘Yan Sandan Najeriya Domin Tunkarar Zabe


A yayinda babban zaben kasa ke kawo jiki a zaben Najeriya rundunar ‘yan sandan kasar na kara daukar matakai domin dakile duk wani rikici da zai iya tashi a lokacin hada hadar siyasar Najeriyar.

A wani taron manema labarai kwamishinan ‘yan sandan jihar Neja Olusola Amore yace a yanzu haka suna gudanar da wani aikin bada horo na musamman ga jami’ansu domin tunkarar siyasar, mataimakin kwamishinan ‘yan sanda Muktar Isiyaku Garko yayi karin haske akan dalilinsu na daukar wannan mataki inda yace, “domin mutum daka turashi gurin aiki baka gaya mishi inda zaiyi ba, to inyaje bazaiyi abinda kagaya masa yayi ba, to amma in yasan abinda zaiyi, farko kafin a fara ya san matsalolin da zai fuskanta kafin a fara kuma yasan matsalolin da zai fuskanta idan ana cikin yin aikin kuma yasan matsalolin da zai fuskanta idan aka gama zaben, to in duk yasan wa dannan abubuwa baza’a samu matsalaba.”

Indai ba’a mantaba zaben shekara ta 2011 ya wuce yabar baya da kura asakamakon tayar da rikici daga wasu da suka nuna rashin gamsuwa da sakamakon.

please wait

No media source currently available

0:00 0:02:37 0:00
Shiga Kai Tsaye

XS
SM
MD
LG