Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Asabar Ake Zaben ‘Yan Mjalisar Dattawa Da Na Tarayya A Nigeria


Mutane suna hutawa karkashin wata gada da aka lillika hotunan 'yan takara a birnin Ikko.
Mutane suna hutawa karkashin wata gada da aka lillika hotunan 'yan takara a birnin Ikko.

Asabar ce ‘yan Nigeria ke dafifi zuwa rumfunan zaben ‘yan majalisar dattawa da na Majalisar wakilan Nigeria, jam’iyyar PDP dake mulkin Nigeria na fatan samun nasarar ci gaba da rike rinjayen da take da shi a zaben, da na shugaban kasa. Masu sanya ido kan yadda ake gudanar da zaben sun yi hassashen ganin ko jami’an hukumar zaben Nigeria zasu iya hana magudi da tashe-tashen hankula dasuka dabaibaye zaben shekarar 2007.

Jami’an hukumar zaben Nijeriya sun yi alkawarin gudanar da zaben wannan shekarar cikin adalci da inganci, kuma sun kawo wasu salon kada kuri’a da nufin magance magudi da kuma kawar da rudami.

Alhamis da ta gabata ce, wata jam’iyyar hamayya a Nigeria dake yankin Naija Delta mai arzikin man fetur ta zargi jami’an tsaro da tsangwama bayan an tuhumi wani wakilinta da laifin cin amanar kasa da kisan kai.

An zargi John James Akpanudoedehe, dan takarar gwamnan jihar Akwa Ibom da laifin cin amanar kasa a makon jiya bayan wani tashin hankali tsakanin magoya bayan jam’iyyarsa ta CAN da na PDP. An bada belinsa ran Alhamis, to amman sai nan da nan kuma aka sake kama shi bisa laifin kisan kai. Magoya bayansa sun ce zargin da ake masa nada alaka da siyasa.

XS
SM
MD
LG