Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Da Dan Gari: Tarihin Garin Tsauri, Katsina


A shirin Da Dan Gari na wannan makon gidan rediyon Vision FM Katsina ya kai ziyara garin Tsauri da ke karamar hukumar Kurfi a jihar Katsina a Najeriya don jin takaitaccen tarihin garin.

Gidado I Abdullahi, shine Maigarin Tsauri, ya ce garin na Tsauri wanda aka kafa a shekarar 1840 ya taba zama gari na biyu a daraja a masarautar Katsina kuma garin ya shahara a fannin ilimi da yaki a zamanin bayan. Hausawa, Fulani, da Bare-bari sune kabilun da aka sani a garin a cewarsa.

Basaraken ya kuma ce asalin sunan garin "Sauki" amma daga baya ya koma "Tsauri."

Saurari cikakken shirin wanda Abdurrahaman Kabir Jani ya gabatar.

Da Dan Gari: Tarihin Garin Tsauri, Katsina
please wait

No media source currently available

0:00 0:07:27 0:00


Facebook Forum

XS
SM
MD
LG