Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Dama Shekarau na Yiwa PDP Aiki – in ji ‘ya’yan APC


APC
APC

Yayin da ‘yayan jam’iyyar PDP a jihar Kano ke murna kan shiga jam’iyyar su da tsohon gwamnan jihar Malam Ibrahim Shekarau yayi, su kuwa mutanen APC A Jihar cewa sukayi Sardaunan na Kano ya tabbatar da zargin da aka yi masa na cewa, dama jam’iyyar PDP yake yiwa aiki.

Wani magoyi bayan Mallam Shekarau mai suna Tasi’u dan Hajiya yace “zan taimaka wa Mallam duk inda yaje a siyasance, shiyasa muke ta kiraye-kiraye akan a yi adalci, a yi sasanto, a zo a tallafawa jam’iyyar nan, a taimaka amma an rufe ido”.

Ita kuwa Aisha Sarka, mai goyon bayan tsohon gwamnan cewa tayi “Mallam Ibrahim Shekarau yana tare da jama’a dari bisa dari, idan hagu yace hagu, idan dama yace dama.”

Tuni dai shuwagabanni da magoya bayan jam’iyyar PDP a jihar Kano suke tsalle da murna, dangane da tagomashin da jam’iyyar tasu, suka ce ta samu.
Alhaji Musa dan Birni yace “Sai muka ji dadi, mun yi Wa Allah godiya kuma jam’iyyata ta PDP ta rabauta yau da babban kamu na Mallam Ibrahim Shekarau. Shigowarsa wannan jam’iyya tawa, ta samu tagomashi kasancewarsa mutumin mutane.

Amma ‘ya’yan APC suma sun tofa albarkacin bakinsu, dangane da wannan sauyin sheka da tsohon gwamnan yayi. Mallam Rabi’u Abdullahi Garin Danga, na hannun daman gwamna Rabi’u Musa Kwankwaso yace “yau dinnan a siyasance, Mallam Ibrahim Shekarau ya fassara kansa a wajen mutanen Kano a siyasance.”

Mallam Garin Danga ya jaddada zargin da ake wa Mallam Shekarau “Daman abunda ake fada, na yana yi wa PDP aiki, ya tabbatar da gaskiya.”

Mallam Ibrahim Shekarau yayi kuka akan shugabancin kama karya na gwamnatin jihar a halin yanzu, shine ya sa yayi sauyin sheka zuwa jam’iyyar PDP, kuma ya kara da cewa akwai mutanen kirki, da na banza a kowace jam’iyya.
Hawan Nasarawa, jihar Kano a Najeriya, lokacin da aka gudanar da bukukuwan Sallar Eid el Fitr
please wait

No media source currently available

0:00 0:03:44 0:00
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA
XS
SM
MD
LG