Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

DOMIN IYALI: Gwagwarmayar Matan Najeriya Da Neman Wakilci A Zaben 2023-Janairu, 26 , 2023


Alheri Grace Abdu
Alheri Grace Abdu

Yau ya rage saura makonni hudu a gudanar da zaben shugaban kasa da na ‘yan Majalisun tarayya a Najeriya, makonni biyu bayan nan kuma a gudanar da na gwamnoni da majalisun jihohi.

Sai dai duk kokarin da mata su ka yi na ganin wannan karon ba a bar su a baya ba, hakar su bata cimma ruwa ba, kasancewa ba su sami wakilcin da suke nema ba.

Batun da zamu fara nazarta ke nan a wannan makon a shirin Yau shirin Domin Iyali.

Bakun da mu ka gayyata domin neman mafita su ne, Hajiya Binta Musa shugabar kungiyar hadin kan mabiya addinai dabam- daban reshen jihar Plato, da Ambassada Rhoda Godwill Jahota, shugabar Kungiyar Mata Kirista a jihar Plato, da Dorcas Lenkat Yusuf shugabar gamayyar Kungiyar Ma’aikatan gwamnati a jihar Plato mai barin gado, sai kuma Ambassada Ridwan Jimat Imam, malami karkashin kungiyar Jama’atu Nasril Islam.

Saurari shirin da wakiliyarmu Zainab Babaji ta jagoranta:

DOMIN IYALI: Gwagwarmayar Matan Najeriya Da Neman Wakilci A Zaben 2023
please wait

No media source currently available

0:00 0:10:36 0:00

  • 16x9 Image

    Grace Alheri Abdu

    Grace Alheri Abdu  babbar Edita ce (Managing Editor) a Sashen Hausa na Muryar Amurka wadda ta shafe sama da shekaru 30 tana aikin jarida. Tana da digiri na biyu a fannin dokoki da huldar diplomasiyar kasa da kasa, da kuma digiri na biyu a fannin nazarin addinan al'adun gargadiya na kasashen Afrika.

XS
SM
MD
LG