Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

DOMIN IYALI: Zargin Magidanci Da Bata 'Ya'yansa Kanana-Kashi Na Uku.


Grace Alheri Abdu
Grace Alheri Abdu

Yau ma zamu dora a bibiya da shirin Domin Iyali ya ke yi kan lamarin da ya faru a Layin Mallam Bello dake garin Kaduna inda wata mace ke neman taimakon al'umma da masu hali baiwa musamman kungiyar lauyoyi mata da kungiyoyin kare hakkin kananan yara domin neman hakinta da na.

Masu saurare dake biye da wannan shirin da dama sun aiko da sakonni ta waya da kuma email suna nuna bayyana niyarsu ta marawa wannan yunkuri na ganin wadannan kananan yara sun zauna a yanayin da zasu samu walwala da rayuwa mai inganci, burin da mahaifiyarsu take nanata a hirarta da Domin Iyali.

Shirin ya samu zantawa da Hajiya Sa’adiya Isa Suleiman, shugabar kungiyar Babajo Disabled and Orghanage Foundation, wadda ta bayyana matakan da suka dauka na taimakawa Fatima dangane da wannan lamarin.

Saurari cikakken shirin

Zargin Magidanci Da Bata 'Ya'yansa Kanana-Kashi Na Uku-!0"
please wait

No media source currently available

0:00 0:10:35 0:00


  • 16x9 Image

    Grace Alheri Abdu

    Grace Alheri Abdu  babbar Edita ce (Managing Editor) a Sashen Hausa na Muryar Amurka wadda ta shafe sama da shekaru 30 tana aikin jarida. Tana da digiri na biyu a fannin dokoki da huldar diplomasiyar kasa da kasa, da kuma digiri na biyu a fannin nazarin addinan al'adun gargadiya na kasashen Afrika.

Facebook Forum

XS
SM
MD
LG