Firayin Ministan Pakistan Shahid Khaqan Abbasi, ya yi shirin kai ziyarar aiki a Afghanistan a yau Jum’a domin tattaunawa a kan dangantakarsu da ta yi rauni da kuma tattaunawa a kan bukatar hukumomi dake Kabul na tattaunawa da Taliban a zaman hanyar kawo karshen rikicin kasar.
Jami’ai a babban birnin Pakistan Islamabad sun ce Abbasi zai kai ziyarar wuni guda ne bisa gayyatar da shugaban Afghanistan Ashraf Ghani ya bashi, a kan neman taimakon Pakistan, ta shiga tsakanin tattaunawa da Taliban.
Shugabannin biyu zasu kuma tattauna a kan kawo karshen tsamin dangantakarsu da kuma hanyoyin bunkasa dangantakar siyasa da tattalin arziki da tsaro da kuma yaki da ta’addanci.
Facebook Forum