Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

GRACE ALHERI ABDU: Domin Iyali, Maris,1, 2018, Bibiya Kan Sace 'Yammatan Dapchi Kashi Na Daya


Grace Alheri Abdu
Grace Alheri Abdu

Ranar Litinin sha tara ga watan Fabrairu 'yan bindiga da ake kyautata zaton 'yan Boko Haram ne suka kai hari a makarantar sakandaren 'yammata dake garin Dapchi, cikin jihar Yobe, suka yi awon gaba da 'yammatan da kawo yanzu gwamnatin tarayyar Najeriya ta tabbatar da sace dari da goma bayanda da farko aka musanta cewa sacesu aka yi. Wannan lamarin dai na faruwa ne bayan kimanin shekaru hudu da sace 'yammatan sakandaren Chibok dari biyu da sab'in da shida a wani lamari irin wannan. Abinda ya dauki hankalin shirin Domin Iyali ke nan wannan mako. Wakilinmu Haruna Dauda Bi'u ya sami zantawa da shugaban kungiyar iyayen da aka sace 'ya'yansu Mallam Bashir Manzo wanda ya fara da bayyana yadda wannan lamarin ya auku, yayinda gwamnan jihar Yobe Ibrahim Gaidam ya bayyana kokarin da jami'an tsaro ke yi na ceto 'yammatan. Saurari bayanansu da kuma wadansu hirarraki a shirin.

Rahoton sace 'yammatan Dapchi-10:30"
please wait

No media source currently available

0:00 0:10:40 0:00

  • 16x9 Image

    Grace Alheri Abdu

    Grace Alheri Abdu  babbar Edita ce (Managing Editor) a Sashen Hausa na Muryar Amurka wadda ta shafe sama da shekaru 30 tana aikin jarida. Tana da digiri na biyu a fannin dokoki da huldar diplomasiyar kasa da kasa, da kuma digiri na biyu a fannin nazarin addinan al'adun gargadiya na kasashen Afrika.

Facebook Forum

XS
SM
MD
LG