Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

GRACE ALHERI ABDU: Domin Iyali, Agusta 23, 2018: Rayuwar Kunci Da 'Yan Najeriya Ke Shiga A Saudiya


Grace Alheri Abdu
Grace Alheri Abdu

Yau shirin Domin Iyali ya yada zango kasar Saudiya, sai dai ba batun aikin hajji zamu nazarta ba. Wannan karon zamu tabo wata matsala da aka dade ana Ambato sai dai kawo yanzu, babu takamammen matakin da aka iya dauka na shawo kan matsalar, Watau batun jan ra’ayin mutane musamman mata da ‘yammata su tafi kasar Saudiya da nufin neman ingancin rayuwa, sai dai idan suka isa wurin su tarar ba haka lamarin yake ba. Wakilin Sashen Hausa Lamido Abubakar yayi kicibis da wannan lamarin yayin aikin hajji da yaje. Ya kuma yi hira da wadanda suke ganau na wannan lamarin, da kuma matakan da hukumomin Najeriya suka fara dauka na shawo kan matsalar.

Saurari cikakken shirin

Halin kunci da 'yan Najeriya ke shiga a Saudiya-10"
please wait

No media source currently available

0:00 0:09:34 0:00

  • 16x9 Image

    Grace Alheri Abdu

    Grace Alheri Abdu  babbar Edita ce (Managing Editor) a Sashen Hausa na Muryar Amurka wadda ta shafe sama da shekaru 30 tana aikin jarida. Tana da digiri na biyu a fannin dokoki da huldar diplomasiyar kasa da kasa, da kuma digiri na biyu a fannin nazarin addinan al'adun gargadiya na kasashen Afrika.

Facebook Forum

XS
SM
MD
LG