Kungiyar ta musanta batun cewa kungiyoyin musulunci basa wa'azi akan illolin kungiyar Boko Haram kamar yadda gwamnan jihar Borno Ibrahinm Shettima ya ambato..
Kungiyar tace wasu malaman addinin musulunci da suka hada da Shaikh Jaafar da Shaikh Albani duk an kashesu ne sabili da bayyana illolin da kungiyar Boko Haram ke haddasawa.
Dr Hassan Abubakar Dikko mai shugabancin shirya gasar karatun Qur'ani na kasa a karkashin kungiyar IZALA yace idan har gwamnan Borno yana ganin kungiyar ta gaza ta wannan hanyar to bibiyarsa ta addinin musulunci ce ta yi kadan domin tsarin kungiyar shi ne duk wata sai ta shirya wa'azi a kasa baki daya. Koina kungiyar na maganar illar Boko Haram har ma a jihohi.
A shekarar 2011 Shaikh Yahaya Jingir ya jagoranci malaman Najeriya gaba daya suka je Maiduguri suka yi wa'azi akan Boko Haram. Wa'azin da suke yi akan kungiyar Boko Haram yana cikin dalilin da ya sa wasu malaman suka rasa rayukansu. Shi kansa Shaikh Jingir an kai masa hari a masallacin 'yan taya a Jos domin yana wa'azi akan 'yan Boko Haram..
Ga karin bayani.