Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Jam'iyar APC Ta Kaddamar Da Kwamitin Sulhu Na Kasa


Membobin kwamitin sasantawa na jam'iyar APC
Membobin kwamitin sasantawa na jam'iyar APC

A hirarsa da Muryar Amurka, shugaban kwamitin rikon kwarya na Jamiyyar Mai Mala Buni ya bayyana cewa,an kafa kwamitin ne domin sasanta mambobin da suka fusata sakamakon za6ukan da aka gudanar a kasar.

shugaban kwamitin rikon ya kaddamar da komitin mutum 9, a karkashin jagorancin dan majalisar Dattawa mai wakiltan jihar Nasarawa ta Yamma Abdullahi Adamu,

Membobin kwamitin sasantawa na jam'iyar APC
Membobin kwamitin sasantawa na jam'iyar APC

Buni ya ce dama akwai korafe korafe daga 'ya'yan jamiyyar daga shiyoyi daban daban na kasar, saboda haka kafa wanan kwamitin hanya ce ta magance su.

A lokacin da yake bayanin matakan da komitin zai dauka wajen yin sulhu musamman ma hada kan 'ya'yan Jamiyyar Shugaban Komitin Sanata Abdullahi Adamu ya bayyana cewa, suna da kwarin guiwa rikicin cikin gida da jam'iyar ke fuskanta a halin yanzu ba zai sa ta sami koma baya a zabuka na gaba ba.

Sauran mambobin komitin su ne tsoffin gwamnoni guda uku, da George Akume na Jihar Binuwai, da Sulivan Chime na Jihar Enugu da Ali Sa'ad Birnin kudu na Jigawa, da tsohon Kakakin Majalisar Wakilai Yakubu Dogara sai Sakataren Komitin Moses Adeyemo.

pdp-ta-amince-da-mika-shugabancin-jam-iyyar-ga-yankin-arewa

abin-da-masana-ke-cewa-kan-zaben-shugabanni-da-apc-ta-yi-a-kananan-hukumomi

za-mu-gudanar-da-tarukan-zaben-shugabanni-duk-da-umarnin-kotu---apc

Saurari cikakken rahoton Medina Dauda daga Abuja:

APC ta kaddamar da kwamitin sasantawa:3:00"
please wait

No media source currently available

0:00 0:02:43 0:00


  • 16x9 Image

    Grace Alheri Abdu

    Grace Alheri Abdu  babbar Edita ce (Managing Editor) a Sashen Hausa na Muryar Amurka wadda ta shafe sama da shekaru 30 tana aikin jarida. Tana da digiri na biyu a fannin dokoki da huldar diplomasiyar kasa da kasa, da kuma digiri na biyu a fannin nazarin addinan al'adun gargadiya na kasashen Afrika.

Hawan Nasarawa, jihar Kano a Najeriya, lokacin da aka gudanar da bukukuwan Sallar Eid el Fitr
please wait

No media source currently available

0:00 0:03:44 0:00
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA
XS
SM
MD
LG