Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Jirgin Farko Ya Tashi Ran Asabar Da Alhazai 500


Jirgin alhazan Najeriya na farko zuwa Saudiyya
Jirgin alhazan Najeriya na farko zuwa Saudiyya

Alhazan Najeriya sun fara tafiya aikin Hajji a kasar Saudiyya

Wakillin Sashen Hausa na shiyar Borno da Yobe, Haruna Dauda Biu ya aiko ma na da rahoton cewa rukunin alhazan Najeriya na farko kimanin dari biyar ya tashi da la'asariyar asabar daga babban filin jirgin saman Maiduguri, jahar Borno. Manyan jami'an da suka halarci kaddamar da tashin jirgin saman na Max Air sun hada da mataimakin shugaban kasar Najeriya Arch. Mohammed Namadi Sambo da gwamnonin Borno da Yobe da Sarkin Musulmi Sultan Sa'ad Abubakar na uku da kuma Shehun Borno wanda shi ne Amirul Hajjin bana. Mataimakin shugaban kasar Najeriya Arch. Mohammed Namadi Sambo ne ya fara yin jawabi kamar haka:

please wait

No media source currently available

0:00 0:02:30 0:00
Shiga Kai Tsaye
XS
SM
MD
LG