Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Kasashen Ketare Zasu Ba 'Yan Tawaye Karin Tallafi


Taron kasashen waje ma'abotan kasar Siriya
Taron kasashen waje ma'abotan kasar Siriya
Sakataren ma’aikatar harkokin wajen Amurka John Kerry yace kasashen turai da kuma kasashen larabawa da suka raba gari da shugaban kasar Siriya Bashar al-Assad sun yi alkawarin kara tallafawa ‘yan tawayen Syria a wani taron da ake kira na ma’abotan Siriya da aka yi a Qatar jiya asabar.

Kerry ya bayyana cewa, ministocin kasashe goma sha daya sun yi alkawarin ba ‘yan tawaye karin tallafin soja da na ayyukan jinkai a yunkurin kawo karshen tashin hankalin tsawon shekaru biyu da ya yi sanadin kashe dubun dubatan Siriyawa.

Kerry yace, yayinda Amurka take kara tallafin da take ba ‘yan tawayen Siriya, hanyar da tafi dacewa da warware rikicin ita ce tattaunawa.
  • 16x9 Image

    Grace Alheri Abdu

    Grace Alheri Abdu  babbar Edita ce (Managing Editor) a Sashen Hausa na Muryar Amurka wadda ta shafe sama da shekaru 30 tana aikin jarida. Tana da digiri na biyu a fannin dokoki da huldar diplomasiyar kasa da kasa, da kuma digiri na biyu a fannin nazarin addinan al'adun gargadiya na kasashen Afrika.

XS
SM
MD
LG