Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Korea Ta Arewa Na Fatan Trump Zai Canza Ra'ayinsa Ya Zauna a Tattauna


Kasar Korea ta Arewa a ta ce har yanzu a shirye take don zaman tattaunawa da Kasar Amurka a kowanne lokaci a kuma duk irin yanayin da take bukata, biyo bayan soke ganawar da shugaban Amurka Donald Trump ya yi da shugaban Korea ta Arewa Kim Jong Un.

Mataimakin Ministan harkokin kasar wajen Korea Ta Arewa Kim Kye Gwan, dadadden mai bada shawarar nukliya kuma babban jami’in diflomasiya, ya fadi a wata sanarwa da wata kafar yada labaran kasar Korea ta Arewa ta watsa, cewa a shirye suke su kara ba Kasar Amurka Karin lokaci don sake tunanin tattaunawar da a da za’ayi a ran 12 ga watan Yunin wannan shekara a kasar Singapore.

Trump ya soke shirin tattaunawa da shugaban kasar Korea ta Arewa Kim Jong Un, inda ya dora laifi akan wasu kalaman barazana da suka fito daga Pyongyang a lokacin da jami’anta suke maida martani akan wasu magangannun da suke dauka kamar na tsokana ne da suka fito daga jami’an Kasar Amurka.

Facebook Forum

XS
SM
MD
LG