Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Nijarf-Kotu To Goyi Bayan Hana Zanga Zanga


Zanga Zanga kan yaki da Cin Hanci da Rashawa a Niamey, Niger,, Disamba 21, 2016 (VOA/Abdoul-Razak Idrissa)
Zanga Zanga kan yaki da Cin Hanci da Rashawa a Niamey, Niger,, Disamba 21, 2016 (VOA/Abdoul-Razak Idrissa)

Kungiyoyin fafaren hula a jamhuriyar nijer sun bayyana shirin daukaka kara, bayanda wata kotun birnin Yamai ta ba ofishin magajin gari gaskiya game da wani matakin hana gudanar da zanga zanga a ranakun aiki wato daga litinin zuwa juma’a saboda dalilan tsaro.

A zamanta na yammacin jiya ne kotun ta bayyana matsayinta dangane da karar da kungiyoyin fafatuka suka shigar a gabanta na bukatar ta dakatar da matakin hanin da Magajin gari ya dauka ta kuma basu damar fita tituna a jiyan kamar yadda suka kudurta a ci gaba da kalubalantar gwamnatin Jamhuriyar Nijar.

Kungiyoyin sun bayyana cewa, suna masu biyayya ga hukumcin kotun, amma zasu dakaka kara zuwa kotu ta gaba.

Kakakin kungiyar Suraju Isa ya bayyana cewa, qa matsayinsu na kungiyoyi masu biyayya da doka, sun yarda da abinda alkaki ya fadi amma wannan ba zai hanasu ci gaba da fafatuka ba. Ya jadada cewa zasu daukaka kara a babban kotu

Yace matakan da hukumomi ke dauka sun tabbatar da korafe korafen da suke yi cewa, damokaradiya ta shiga wani irin hali a Jamhuriyar Nijar. Yace wadannan matakan da ake dauka basu cikin kundin tsarin mulkin kasar.

Kungiyoyin dai sun shiga wannan fafatuka ne da nufin neman gwamnati ta dauki mataki a fannonin ilimi, kowon lafiya, zamantakewa da dai sauransu da suka ce sun jefa al’ummar Jamhuriyar Nijar cikin halin kunci.

Ga cikakken rahoton da wakilinmu Sule Mummuni Barma ya aiko mana daga birnin Nyamie.

Rahoton Hana zanga zanga a Nijar-3:26"
please wait

No media source currently available

0:00 0:03:26 0:00

  • 16x9 Image

    Grace Alheri Abdu

    Grace Alheri Abdu  babbar Edita ce (Managing Editor) a Sashen Hausa na Muryar Amurka wadda ta shafe sama da shekaru 30 tana aikin jarida. Tana da digiri na biyu a fannin dokoki da huldar diplomasiyar kasa da kasa, da kuma digiri na biyu a fannin nazarin addinan al'adun gargadiya na kasashen Afrika.

XS
SM
MD
LG