Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Kungiyar Mata Musulmi ta Najeriya "MSO" ta yi Babban Taro Mai Taken "Hadin Kan Musulmi da Kalubalen Karni"


wasu mata Musulmi a Najeriya
wasu mata Musulmi a Najeriya

Shugabar kungiyar ta mata Musulmi Hajiya Salamatu Ibrahim ta ce rabe-raben kan Musulmai yayi yawa a ma duniya baki daya

Kungiyar mata Musulmi ta kasar Najeriya, Muslim Sisters Organization, MSO a takaice, ta yi taron ta na shekara-shekara a Kaduna. Taken taron na bana shi ne "Hadin Kan Musulmi da Kalubalen Karni". Wakilin Sashen Hausa a Kaduna Isah Lawal Ikara ya halarci taron kuma ya fara ne da tattaunawa da shugabar kungiyar ta kasa Hajiya Salamatu Ibrahim:

please wait

No media source currently available

0:00 0:03:00 0:00
Shiga Kai Tsaye


Sheikh Ahmed Gummi na cikin manyan masu jawabai a wurin taron kuma ya ce babban kalubalen Musulmi shi ne jahilci, idan da ilimin addini da na duniya babu wata matsala. Ita ma malama Rabi'at Ahmad Sufian shugabar kungiyar tallafwa mata Musulmi a Najeriya ta ce muddin mata suka gyaru to al'umma ta gyaru.
XS
SM
MD
LG