Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

NANS Ta Gana Da Sheikh Gumi Kan Yadda Za A Ceto Daliban Da Aka Sace


Tawagar daliban Najeriya a ziyarar da suka kai wa Sheikh Gumi.
Tawagar daliban Najeriya a ziyarar da suka kai wa Sheikh Gumi.

“Za mu ci gaba da tattaunawa da masu ruwa da tsaki don tabbatar da tsaro a makarantu.” Shugaban na NANS ya ce.

Kungiyar daliban jami’o’in Najeriya NANS, ta kai wa Sheikh Ahmad Gumi ziyara a jihar Kaduna da ke arewa maso yammacin kasar.

Wata sanarwa da shugaban kungiyar Sunday Asefon ya wallafa a ranar Litinin ta ce, tawagar daliban ta tattauna da Shehin malamin kan al’amuran da suka shafi kare lafiyar daliban Najeriya a duk jami’o’i da kuma matakan da za a bi don sako wadanda aka yi garkuwa da su.

“Mun yi magana kan yadda za a ci gaba da tattaunawa dangane da yadda za a sako daliban da aka sace da kuma matakan da ya kamata a bi wajen ganin an tabbatar da cewa makarantu suna da cikakken tsaro.

Shugaban NANS, Sunday Asefon (hagu) da Sheikh Gumi (dama) (Facebook/NANS)
Shugaban NANS, Sunday Asefon (hagu) da Sheikh Gumi (dama) (Facebook/NANS)

Karin bayani akan: Zaria, jihar Neja, Sheikh Ahmad Gumi, Shugaba Muhammadu Buhari, Nigeria, da Najeriya.

“Saboda dalibanmu su gujewa fargabar yiwuwar a yi garkuwa da su.” Asefon ya ce.

“Za mu ci gaba da tattaunawa da masu ruwa da tsaki don tabbatar da tsaro a makarantu.” Shugaban na NANS ya ce.

A ‘yan watannin baya Sheikh Ahmad Gumi, ya kan shiga daji don ya yi wa 'yan fashin dajin wa'azi tare da sauraren korafe-korafensu.

A baya-bayan nan ‘yan bindigar sun sace dalibai da malamai a kwajelin kimiyya da fasaha ta Nuhu Bamalli da ke garin Zaria.

Kazalika sun sace dalibai sama da 100 a wata makarantar Islamiyya da ke garin Tegina a jihar Neja.

Sannan sun yi garkuwa da daliban sakandaren gwamnatin tarayya da ke Yawuri a jihar Zamfara.

Har yanzu ba a jin duriyar dukkan wadannan dalibai da aka sace.

‘Yan bindigar kan nemi a biya su miliyoyin kudade kafin su saki mutanen da suka yi garkuwa da su a Najeriya.

Hukumomi a matakin jiha da tarayya sun ce suna iya bakin kokarinsu wajen ganin sun magance matsalar tsaron musamman wacce ta shafi satar mutane don neman kudin fansa.

Hawan Nasarawa, jihar Kano a Najeriya, lokacin da aka gudanar da bukukuwan Sallar Eid el Fitr
please wait

No media source currently available

0:00 0:03:44 0:00
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA
XS
SM
MD
LG