Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Amurka Ba Za Ta Fasa Fada a Afghanistan Ba - Jim Mattis


Birnin Kabul ne wuri na biyu da Mattis ya je a ziyarar da yake yi a kasashen yanken kudancin Asiya, bayan da ya fara zuwa New Delhi, babban birnin kasar India.

Sakataren harkokin tsaron Amurka Jim Mattis ya ce Amurka, da sabuwar dabarar da ta fito da ita ta warware kiki-kakan da aka yi da mayakan kungiyar Taliban, ba zai sa ta daina fada a Afghanistan ba.

‘Yan sa’o’i bayan isarsa kasar, wani harin roka da aka kai a tashar jiragen saman birnin Kabul ya raunata mutane 5.

Sakataren rundunar NATO Jens Stoltenberg, wanda shima ya je birnin na Kabul, ya jaddada kudurin NATO na taimakawa Afghanistan.

Shirin da shugaba Donald Trump ya fidda akan Afghanistan, cikin watan da ya gabata, ya nuna irirn gagarumar rawar da kasashen yanken zasu taka ciki harda India.

Facebook Forum

XS
SM
MD
LG