Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Samu Ingantacen Zabe sai an Baiwa Kananan Hukumomi Cikakken ‘Yancin


A daidai lokacin da ake shirin tunkarar zabubbukan shekarar 2015.

A daidai lokacin da ake shirin tunkarar zabubbukan shekarar 2015 a Najeriya, kungiyar ma’aikatan kananan hukumomi, NULGE, ta na tabbatar wa da duniya cewa, babu yanda za’a, samu ingantacen zabe, sai an baiwa kananan hukumomi, cikakken ‘yancin gashin kansu a Najeriya.

Shugaban kungiyar NULGE, na kasa Komrade Ibrahim Khalid, ne ya bayana haka a lokacin da yake amsa tabayoyi ‘yan jaridu, a garin Kaduna.

Ya kara da cewa, hatta jagwalgwalon, zaben fita gwanin da ake samu a jamiyun kasar nan ba wani abu ya kawo suba illa sakacin da aka samu na kin baiwa kananan hukumomi, ‘yancin gashin kansu, alhali kuwa sune a sashin baiwa aluma, cikakken baiwa aluma, cikakken ‘yancin zaben shuwagabaninsu.

Gamai da sabubbuka shekarar 2015, kuwa komrade Ibrahim Khalid, yace irin abubuwan da akayi a zaben fidda gwani, ne za’a sake kwatantawa.

Samu Ingantacen Zabe sai an Baiwa Kananan Hukumomi Cikakken ‘Yancin - 3'48"
please wait

No media source currently available

0:00 0:03:48 0:00

XS
SM
MD
LG