Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Shugabannin Sudan ta Kudu Sun Yi Watsi da Kafa Kotu Na Musamman


Mataimakin Shugaban Sudan ta Kudu Na Daya Riek Machar, da Shugaban Kasa Salva Kiir
Mataimakin Shugaban Sudan ta Kudu Na Daya Riek Machar, da Shugaban Kasa Salva Kiir

Jaridar New York Times ta nan Amurka ta wallafa wata makala da shugaban Sudan ta kudu da Salva Kiir, da abokin hamayyarsa Riek Macher, wanda yanzu shine mataimakin shugaban kasa na farko, suka rubuta, inda dukkansu biyu suka bayyana adawarsu kan shawarar kafa wata kotu ta musamman wacce zata kun shi 'yan kasar da ma na kasashen waje.

Manufar kotun shi ne ta hukunta wadanda ake zargi da aikata munanan laifuffukan yaki daga duka bangarorin biyu, sakamkon yakin basasar da kasar tayi fama da shi na tsawon shekaru biyu.

Duk da cewa kafa irin wannan kotun yana cikin sharuddan yarjerjenoiyar zaman lafiya da duka shugabannin biyu suka sanya hannu kai. Saboda haka wanan makala ta janyo cecekuce a cikin kasar.

Amma kakakin shugaba Salva Kiir,ya kare makalar, yana mai cewa, kafa wannan kotu zai zake maida kasar cikin tarzoma.

Amma wani dan rajin kare 'yancin Bil'Adama Edmund Yakani, yace makalar wani yunkuri ne da wadanda suka aikata laifuffukan yaki kuma suke cikin gwamnati suke dauka domin kaucewa hukunci. Yace muddin ba'a hukuntasu ba za'a ci gaba da karya doka.

Hawan Nasarawa, jihar Kano a Najeriya, lokacin da aka gudanar da bukukuwan Sallar Eid el Fitr
please wait

No media source currently available

0:00 0:03:44 0:00
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA
XS
SM
MD
LG