Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Sun Dauka na Mutu Suka Jefar Da Ni A Cikin Jeji


irin matasan da ke shiga kungiyar Boko haram wadanda yawancin su ke fadawa hannun jami'an tsaro
irin matasan da ke shiga kungiyar Boko haram wadanda yawancin su ke fadawa hannun jami'an tsaro

Babu alamun aikin Allah a Boko Haram, inji dan kungiyar da ya kubuta, ya ce sai kisa da kwacen dukiyar jama'a

Wani matashi dan shekara ishirin da biyu da haihuwa ya tona asirin kungiyar Boko Haram. Matashin dan Boko Haram ne wanda jami’an tsaro suka tsinta jina-jina a jeji a yashe bayan wani harin da suka kai garin Damboa, a tazarar kimanin kilomita tamanin da bakwai da Maiduguri, jahar Borno. Bayan ya koma cikin hayyacin shi ya yiwa kungiyar ta Boko Haram fallasa da tonon sililin cewa jihadin da kungiyar ke ikirarin yi karya ta ke yi, ba jihadin da take yi illa ci da addini, ya ce ba abun da ‘yan kungiyar ke aikatawa sai kashe-kashen keta da azabtar da al'umma da kwace musu dukiya. Wakilin Sashen Hausa a jahar Borno, Haruna Dauda Biu ya yiwa matashin tambayoyin da ya fara yi kamar haka:

Dan Boko Haram na tona asirin kungiyar - 5:51
please wait

No media source currently available

0:00 0:05:51 0:00
Shiga Kai Tsaye
Hawan Nasarawa, jihar Kano a Najeriya, lokacin da aka gudanar da bukukuwan Sallar Eid el Fitr
please wait

No media source currently available

0:00 0:03:44 0:00
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA
XS
SM
MD
LG