Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Tsaro: Shirin Bayyanar Buhari Gaban Majalisa Gobe Ya Fara Janyo Muzurai


Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari.
Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari.

A wani al'amari mai kama da somin tabin abin da ka faru idan Shugaban Najeriya ya bayyana gaban mafusatan 'Yan Majalisar Tarayyar Kasar saboda matsalar tsaro, tuni aka shiga takaddama kan yanayin gayyatarsa da kuma tsarin zaman da za a yi.

Yayin da ake jiran bayyana da aka ce Shugaba Muhammadu Buhari zai yi a gaban Majalisar Tarayyar Najeriya gobe Alhamis, tuni aka fara jayayya kan tsarin bayyanar da kuma salon ba’asin da zai bayar game da tabarbarewar tsaro a Najeriya.

A wani mataki na warware zare da abawa a harkar tsaro da ke addabar Najeriya ne Majalisar Wakilai ta gayyaci Shugaban Kasa Muhammadu Buhari da ya bayyana a gabanta domin amsa tambayoyi, kuma Shugaban Kasa ya amsa kira. To saidai wasu ‘yan Majalisar na ganin ba za a wanye lafiya ba, saboda ‘yan Majalisar sun fusata, musamman ma ‘yan adawa da ke kiran da a tsige Shugaban kasar.

Muhammadu Buhari
Muhammadu Buhari

Wannan gayyata da Majalisar Wakilai ta yi wa Shugaba Mohammadu Buhari ita ce irin ta na farko tunda ya hau karagar mulki a shekara 2015.

Gayyatar ta biyo bayan kudurin doka ne da wasu mambobin Majalisar daga jihar Barno suka gabatar akan kisar gillar da 'yan Boko Haram suka yi ma wasu manoma akalla 43 a jihar..

To saidai duk da cewa Shugaba Buhari ya amsa gayyatar kuma har an sa rana - cewa gobe Alhamis ne bayyana, amma al'amarin yana neman daukar sabon salo domin an ce ba Majalisar Wakilai kadai zai je ba, za a yi zaman hadin gwiwa ne da Majalisar Dattawa, wani abu da Shugaban Masu Rinjaye a Majalisar Dattawa ya ce akwai abin dubawa, domin ya kamata a aiko da wasika zauren Majalisar dattawa akan hakan, a kuma karanta ta kowa ya amince tukuna, in ba haka ba zaman, to hadin gwiwa zai yi wuya.

A screengrab taken on July 13, 2014 from a video released by the Nigerian Islamist extremist group Boko Haram and obtained by AFP shows the leader of the Nigerian Islamist extremist group Boko Haram, Abubakar Shekau (C). The head of Nigeria's Boko Haram…
A screengrab taken on July 13, 2014 from a video released by the Nigerian Islamist extremist group Boko Haram and obtained by AFP shows the leader of the Nigerian Islamist extremist group Boko Haram, Abubakar Shekau (C). The head of Nigeria's Boko Haram…

A lokacin da yake nashi nazarin, Shugaban Kwamitin Kula da Harkokin Sojin Sama a Majalisar Wakilai, Shehu Mohammed Koko ya ce ba daidai ba ne Majalisar Wakilai ta yi kuduri na gayyatar Shugaban kasa, amma kuma a hada su da Majalisar Dattawa. Ya ce shi baya goyon bayan gayyatar, domin Shugaban Kasar ba zai fadi wani abu daban da wanda shugabanin hukumomin tsaro ke fada kullum ba. Koko yana ganin abinda ya dace kawai shi ne a zauna da shi cikin sirri domin haka harkar tsaro ta gada.

A wani abu mai kamar mayar da martani, Shugaban masu rinjaye a Majalisar Dattawa, Sanata Yahaya Abdullahi Abubakar, ya ce kafin a yi zaman hadin gwiwa sai Majalisun biyu sun amince tukuna, kuma a irin wanan yanayi da wasu ke nuna fushi da abubuwan da ke faruwa a kasa, yana ganin barin yin taron gaba daya zai fi, inda ya bada shawarar Shugaba Muhammadu Buhari yayi wa kasa jawabi ta kafafen yada labarai.

FILE - This view shows one of the biggest camps for people displaced by Islamist extremists in Maiduguri, Nigeria, Aug. 28, 2016. The U.N. Security Council on March 3, 2017, kicked off a visit to spotlight Africa's worst humanitarian crisis as millions fa
FILE - This view shows one of the biggest camps for people displaced by Islamist extremists in Maiduguri, Nigeria, Aug. 28, 2016. The U.N. Security Council on March 3, 2017, kicked off a visit to spotlight Africa's worst humanitarian crisis as millions fa

Tun dai a daren jiya Talata ne Shugaba Muhammadu Buhari yake ta tarurruka da Gwamnoni akan batun tsaron kasa. Abin jira a gani shi ne ko sakamakon tarurrukan zai sa Shugaba Muhammadu Buhari ya canja ra'ayinsa a game da zuwa Majalisar, lokaci ne kadai zai baiyana haka.

Ga Madina Dauda da cikakken rahoton:

please wait

No media source currently available

0:00 0:02:56 0:00


Hawan Nasarawa, jihar Kano a Najeriya, lokacin da aka gudanar da bukukuwan Sallar Eid el Fitr
please wait

No media source currently available

0:00 0:03:44 0:00
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA
XS
SM
MD
LG