Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Tsohon Shugaban Babban Bankin Najeriya Emefiele Zai Fuskanci Sabon Tuhuma


Emefiele
Emefiele

A yau Litinin ne tsohon gwamnan babban bankin Najeriya, Godwin Emefiele, zai gurfana a gaban wata kotu a Lagos bayan hukumar yaki da cin hanci da rashawa ta kasar a ranar Juma’a ta shigar da wasu sabbin tuhume-tuhume har guda 26 da ake zarginsa a kansu na aikata zamba da kuma cin hanci da rashawa.

Tuni dai Emefiele ke fuskantar tuhumar zamba a wata kotu a Abuja babban birnin kasar - wanda ya musanta - bayan tsare shi a watan Yunin bara da Hukumar Tsaron Farin Kaya ta DSS ta yi. Daga baya aka mayar da shi hukumar yaki da cin hanci da rashawa da yi wa tattalin arzikin kasa zagon kasa, kuma an bayar da belinsa a watan Nuwamba.

Tuhume-tuhumen na baya-bayan nan sun hada da karbar cin hanci, karbar kyaututtuka, da aikata almundahana, da mallakar dukiyoyin gidaje ta hanyar rashin gaskiya, da samar da wasu damarmaki ma abokansa wadanda ba su cancanci samu ba, kamar yadda takardun kotu su ka nuna.

Godwin Emefiele a kotu
Godwin Emefiele a kotu

Da aka tuntubi wani mai wakiltar Emefiele wajen shari’ar bai amsa bukatar jin ta bakinsa ba kan sabbin tuhume-tuhumen da aka yi masa ranar Asabar.

A ranar 9 ga watan Yuni ne dai shugaba Bola Tinubu ya dakatar da tsohon gwamnan babban bankin kasar, sannan aka kama shi kwana guda bayan hakan. Ya yi murabus ne a watan Agusta, inda ya share fagen nada sabon gwamna Olayemi Cardoso a watan Satumba.

A ranar Juma’a wani mai bincike na musamman da shugaba Tinubu ya dauka domin ya binciki babban bankin kasa karkashin Emefiele ya ce ya kammala aikinsa. Ba a bayyana rahoton nasa ba.

Dandalin Mu Tattauna

XS
SM
MD
LG