Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Yau Ce Ranar Matasa Ta Duniya


Taron Karfafa Gwiwar Yaki Da Cin Hanci Da Rashawa A Abuja Ya Sami Halartar Matasa Da Dama
Taron Karfafa Gwiwar Yaki Da Cin Hanci Da Rashawa A Abuja Ya Sami Halartar Matasa Da Dama

12 ga watan Agusta, rana ce da Majalisar Dinkin Duniya ta ware domin yin dubi kan irin halin da matasa ke ciki.

Abubuwan da akan duba sun hada da irin gudunmuwar da matasa ke bayarwa wajen ci gaban kasa da kuma irin kalubalen da su ke fuskanta a rayuwa, musamman wadanda su ke zama masu cikas wajen cimma burinsu.

Taken wannan sheraka ta 2016 shi ne “Hanyar kai wa ga muradun 2030: Kawar da talauci da tabbatar da dorewar hanyoyin masu amfani da samar da ababan rayuwa.”

A ranar 17 ga watan Disambar 1999 Majalisar Dinkijn Duniya ta amince da kebe wannan rana ta matasa.

A Najeriya, wakilinmu Muryar Amurka, Babangida Jibril, ya yi dubi kan wannan rana ga kuma rahoton da ya aiko mana daga Legas a kudu maso yammacin Najeriya:

please wait

No media source currently available

0:00 0:02:20 0:00
Shiga Kai Tsaye

XS
SM
MD
LG