An kama kakakin kungiyar Boko Haram

  • VOA Hausa

Boko Haram

Wani jami’in yan sandan ciki na Najeriya yace an kama kakamin kungiyar Boko Haram da ake dorawa alhakin hare haren da suka yi sanadin kashe daruruwan mutane a arewacin Najeriya.

Darektan yan sandan ciki na jihar Borno ya shaidawa manema labarai cewa, an kama kakakin da ake kira Abul Qaqa a Maiduguri. Darektan ya bayyana cewa, an kama Abul Qaqa ne ta wajen bin sawun wayarshi ta salula, ya kuma bayyana cewa, kakakin kungiyar dan Najeriya ne wana.

Aika Sharhinka